Tasirin sunayen Allah A Duniya

Islamkingdom_ar01 Dec, 2019Religion

Dangane da waxanda suka ce Allah zai daidaita tsakanin abubuwan da suka sava da juna, kamar masu biyayya da masu fajirci, ko muminai da kafirai, Allah ya ce : �Waxanda suka yi munanan ayyuka suna zaton za mu sanya su kamar waxanda suka yi imani kuma suka yi ayyuka na qwarai, daidai ne mutuwarsu da rayuwarsu, abin da suke hukuntawa ya yi muni� (al-jaasiya : 21) Allah ya ba da labarin cewa hukuncinsu mummuna ne, sunayen Allah da siffofinsa ba za su xauki haka ba, Allah ya ce, �Yanzu kuna zaton mun halicce ku don wasa ne, kuma ba za ku dawo wajenmu ba. To Allah ya xaukaka sarki na gaskiya, wanda babu wani abin bautawa da gaskiya sai shi, Ubangijin Al�arshi mai girma� (Almuminuna : 115 � 116) Allah ya xaukaka daga zaton masu mummunan zato, wanda sunayen Allah da siffofinsa ba za su xauke shi ba. Irin wannan yana nan da yawa a cikin Alqur�ani. Allah yana korewa kansa savanin abin da sunayensa da siffofinsa suka nuna, domin hakan yana rushe kamalar su ne da ma�anoninsu.

Recent Profiles

Addilyn Amalia

Addilyn Amalia

View Profile

Cosmic Scanner

Cosmic Scanner

View Profile

Nhà cái 789BET

Nhà Cái 789bet

View Profile

KK55 KK

Kk55 Kk

View Profile

tr886org1

Tr886org1

View Profile

188Bet

188bet

View Profile

betu888org

Betu888org

View Profile

İstanbul Vita

İstanbul Vita

View Profile

Business

Business

View Profile